Siyasar Musulunchi

Shafin Farko | ENGLISH PAGE | Shafukan malamai | Littafin maziyarta | Hotuna | Tuntuba | Siyasar Muslunchi | Shahidan Karbala | Photoalbum

Jagoran Harka Islamiyya Sheikh Zakzaky

SABUWAR GABAS TA TSAKIYA: INA AKA KWANA?

 

Tsohuwa jawarar nan ta kasa Amurka, kuma ‘yar amshin shatan Amurka Mr. Bush, wadda kuma ake kira a gabas ta tsakiya da “Hammalatul hadab” ko kuma in yi barobaro nace ina nufin Condelezza Rice, a cikin watan Yuli ne ta bayyana cewa yakin da ake tsakanin Hizbullahi da Isra’ila wani yunkurine na haihuwar wata sabuwar gabas ta tsakiya.

 

Tun kafin wannan yaki da Haramtacciyar Kasar Isra’ila (HKI) tayi da baradan nan Hizbullahi akwai wasu alamomi da suka nuna Amurka da kawayenta suna da wani mummunan kuduri ga yankin, sai kuma gashi ta bayyana cewa shirin yana da nasaba da haihuwar sabuwar gabas ta tsakiya ne. Sai dai abin tambaya shine; mi suke nufi da sabuwar gabas ta tsakiya ne? Wannan ya yiwu itace tambayar da mafiya yawan jama’a suka rinka yi bayan jin waccan manufa.

 

Sabuwar gabas ta tsakiya, ko faffadar gabas ta tsakiya, suna nufin gabas ta tsakiya mai dauke da zallan mulaka’u (masu mulki) ‘yan amshin shatan Amurka, kawar da dukkan malamai masu yunkurin raya addinin musulunci a zukatan al’umma, share duk wata gwagwarmaya ta neman ‘yanci, kawar da duk wasu masu kishin adddinin musulunci a yankin tare da share tasirin addinin musulunci a zukatan al’ummar yankin, share duk wasu alamomin addini ko da kuwa gine-gine ne a yankin, samar da damar tatse arzikin yankin musamman man fetur da Allah Ya albarkaci yankin da shi, sanya wa al’ummar takunkumi a bakunan mutanen yankin musamman ta fuskacin siyasa, ci gaba da addini, samar da biyayya ga sabon musuluncin da Amurka ke shirin haihuwa, kauda dogaro da kai ga mutanen yanki, dawwamar da HKI a yankin ba tare da daga mata ko da yatsa ba daga wata kasa, fadada HKI a yankin ta hanyar mamaye kasashen makwabtanta kamar su Lebanon, Palasdinu, Siriya, Jordan, Iraki dss, samar da ‘yan siyasa kuma ‘yan koren Amurka wadanda a shirye suke su saida mutuncin al’ummarsu kamar dai su Kharzai ( samar da wasu kharzanonin a sauran kasashen musulmi irin su Palasdinu, Lebanon da Iraki, dss).

 

Wannan yunkuri na haihuwar sabuwar gabas ta tsakiya ya fara fitowa a fili ne tun lokacin da aka shirya hari akan dogayen gine-ginen Amurka da “pentagon” ran 11 ga satumban 2001. Wannan ya haifar da haihuwar Osama bin Laden da kungiyar nan tasa AlQa’ida da C.I.A.(kungiyar leken asirin Amurka) ta haifa a cikin labule. Bayan faruwar al’amarin ne sai Mr. Bush (wanda shugaban kasar Venezuela Hugo Chavez ya kira da shaidani) yace zai yi yakin “Crusade”  sakamakon wannan harin, idan aka duba “dictionary” ma’anarsa shine yakar addinin musulunci. Kalaman nasa sun yadu a kafafen yada labarai.

 

Wannan ya haifar da Amurka ta jagoranci munanan kashe kashen rayuka masu yawan gaske , azabtarwa, kame-kame, rushe-rushen gidaje, ruwan bama bamai akan fararen hula da yawansu mata da yara da tsofaffi a  kasashen Afganistan da  Iraki, a gefe guda kuma ga Israila na cin karenta babu babbaka a kasashen Palasdinu da Lebanon an kuma hana wata kasa tayi mata koda harara.

 

An dai yi ta ruwan bama- bamai a yankin tun daga bayan satumban 2001 kama daga bama baman “nail bomb”, “chemical bomb”, “cluster bomb”, “uranium bomb” da makamantansu. Amurka tamaida yankin wata cibiyar hada hadar makamai ita da kawayenta, a yayinda HKI ma ta amshi nata tallafin makaman don wancan kuduri daga hannnun Amurka a watan Yuli 2006 a matsayin karin kaso. Haka ma a ranar 25 ga watan yulin jiragen Amurka biyar ne suka tashi daga sansanin sojin Amurka na Saudiyya da Qatar dauke da ton ton na mugayen makamai don kai tallafi ga HKI . Bayan wadan nan ma wasu jiragen dauke da makamai har yada zango sukayi don hutawa daga Amurka akan hanyarsu ta zuwa HKI.

 

A lokacin da aka sanya wa Jamhuriyar Musulunci ta Iran karan tsana da barazana kan shirinta na makamashin nukiliyar zaman lafiya ita HKI nada damar kera wadancan mugayen makamai kuma an hana hukumar binciken ta IAEA da ce mata uffan a makerarta dake Dimona kusan sama da shekaru 40.

 

A duk lokacin da HKI ta kai farmaki kan raunannan al’ummar fararen hulan Palasdinu ko Lebanon sai Amurka da kawayenta suce tana kare kanta, a yayinda sukuma musulmin yankin aka hana masu wannan ‘yanci na kare kai. In kuwa har suka maida martani to sunansu “yan ta’adda” “tsageru” “masu tsattsauran ra’ayi” “masu zazzafan ra’ayi” da makamantansu kuma a shelanta cewa kawar da su ya zama wajibi, kuma dole ne kowa ce kasa ta taimaka a kan haka, ciki kuwa harda NATO da kasashen larabawa. Wannnan dai duk yana da nasaba da yunkurin haihuwar ita waccan sabuwar gabas ta tsakiya ne.

 

Sai dai Bush da Hammalatul Hadab (condalezza) sun yi aman da suka shelanta wa duniya sunyi shi kuma suka kwashi daagwalonsa suka kai wasu kasashe lokacin da rundunar Hizbullahi suka bayyana kama sojojin HKI 2 da kashe 8 a lokacin da suka shigo yankin kudancin Lebanon don ayyukan ta’addanci kamar yanda suka saba. Kowa ya sani cewa HKI ba tana tura sojojinta makwabtanta bane don samar da zaman lafiya, sai dai faruwar hakan ya basu damar su bayyana wa duniya wannnan mafarki da suke na haihuwar waccan cikin shege da suke kokarin haihuwa. Wani abu shine, an dai gwabza yaki, anyi gumurzu, anyi ruwan bama-bamai da rokoki har na tsawon kwana 34 amma waccan nakuda bata kare ba, ina ma tunanin yanzu sun gano cewa wancan cikin fa ya zube kuma ba za’a taba samun wani ba matukar akwai dakaru tsayayyu irin Hizbullahi da Hamas (da tace sambata yarda da kasantuwar HKI ba) a yankin, ko akwai irinsu AhmadiNejad na Iran ko su Muqtada As Sadr a Iraki. Duk manufofin da aka ce sune dalilin wancan yaki ba a cimma ko da daya ba, Misali maganar kwato sosjojin HKI biyu har aka gama ba a amsosu ba, kamar yanda Sayyid Nasrullah yace duk duniyar nan babu  karfin da zai iya kwato su sai dai ta hanyar tattaunawa ta shiga tsakani, kuma har yanzu a haka ake. Haka ma manufar da suka shelanta na gusar da Hizbullahi daga kudancin lebanon ko kuma raba su da makamai, kafin ma a dakatar da wuta yawan makaman da Hizbullahi suka rinka harbawa yafi na farkon fara yakin.

 

Su kuwa dakarun HKI musamman wadanda akewa kirarin da babu kamarsu a duk yankin “Golani Brigade” sai da suka kawshi hannunsu a hannu ta yanda suka rinka gudu suna barin filin daga, ance don bakin cikin wannnan rashin nasara yasa daga baya wasu ma cikinsu suna kashe kansu. Tankar nan ta Merkava kirar HKI da take da tsada da kwarjini a kasashen duniya ta wulakanta a hannun Hizbullahi ta yanda rokokinsu ke mata dai dai. Wannan ya nuna wancan ciki ya gamu da mummunar nakudar da za a dade ba a daina jin radadinta ba, kuma za a dade ba a kara tunanin samar da irin wancan ciki ba. Yanzu dai ya zube, ya bare kuma ya daidaice warwas. Sai dai tarihi ya tuno da abin da suka faru a lokacin nakudar cikin da Hizbullahi suka yi barinsa.   

 

A wancan lokacin sojojin HKI sun yita jefa takardun gargadi ga al’ummar kudancin Lebanon wai su fice daga gidajensu in kuma sunki to munanan hare-haren da zasu mai a yankin zai shafesu. Tayiwu sun so share yankin ne don samar da sababbin mazaunan yahudawa ‘yan share wuri zauna kamr yanda suke yi a Palasdinu kamar garuruwan kewayen Gaza, Rafah da Al Areesh. Amma wani abin ban sha’awa, mazauna yankunan na kudancin Lebanon suka ce ba inda zasu, ba domin komi ba sai don kudurin cewa ai sojojin Hizbullahi ‘ya’yansu ne duk abinda zai samesu to ya same su tare. Wannan bai yiwa HKI dadi ba shi yasanya ma suka dinga harba mugayen bama-bamai a gidajen da suke tunanin an tara yara, mata da tsofaffi, kamar harin zaluncin da suka kai a garin Qana wanda yayi sanadiyyar shahadar mutum wajan 60 mafiya yawa mata da yara.

 

Ta daya bangaren kuma, ba zamu manta da gudunmuwar da wasu shugabannin kasashen larabawa suka bada ba a wajan yunkurin nakudar haihuwar wannan cikin shegen Mr. Bush da ya bare. Wannan kuma yana da nasaba da halayyarsu ta munafuntar juna da kuma watsi da adddinin musulunci tare da kokarin kare kujerar sarautarsu ta kowa ce hanya. Mr. Bush yana kiransu ya yi masu jankunne na musamman, kuma yana yi masu kurari da mazurai akan su tullafawa duk shirinsa a yankin gabas ta tsakiya. Ko a watan satumba 2006 lokacin taron majalisar dinkin duniya, shugaban Pakistan Musharraf ya fada wa manema labarai a Amurka cewa Mr. Bush yace masa indan bai taimaka a kan yakin da ake da Afghanistan ba to shima zai kai masa hari. A duk yankin gabas ta tsakiya jamhuriyar Musulunci ta Iran ce kawai sai Siriya kasar Amurka da HKI suke saurara wa shugabanninsu don kuwa shima Mr. Bush ya samu labari tun daga kakanninsa cewa wadan nan kasashe ba zasu taba rankwafawa zaluncin shaidanun duniya ba. Dalilin kuwa baya rasa nasaba da cewa sune ake da tabbacin suna da shugabanni a mafiya yawan kasashen yankin wadanda masu mulkin kaar basu da salsalar jini da yahudawa.

 

A Kasar Masar, wanda akewa kirari da “sa mai dariyar keta” Hosni Mubarak lokacin wancan fafatawa da dakarun na Hizbullah cewa yai “ Masar ba zata yi fada da Israila ba saboda Hizbullah, na kuma tabbatar da Israila ba zata yaki da Masar ba”. Haka kuma, Masar din ta bada mashigar hanyar ruwan nan na “Suez Canal” don bada dama ga Amurka ta wuce da jiragen makamanta na tallafi ga HKI, an ruwaito cewa a ranar ma, an hana duk wata zirga-zirga a yankin don farantawa a Amurka da HKI.

 

Saudiyya kuwa, har su “Sheikh” (sahibul shirk wal haram) suka fitar da fatawa bisa umarnin gwamnatin kasar don farantawa iyayen gidansu. Fatawar da Sheikh Abdullah bin Jibrin cewa tayi “haramun ne a goyi bayan Hizbullahi ko a yi masu fatar samun nasara.” Manya kaji masu addini.

 

Masarautar Jordan kuwa har mitin suka gudanar a asirce da HKI don nuna masu goyon bayansu a wannan yaki. Ga kuma labaran da suka fito cewa gwamnatin Amurka na tafiyar da wasu gidajen yarin asiri a kasar da tallafin masarautar ta Jordan.

 

Tarayyar Daular Larabawa U.A.E. da Kuwait duk sun bayyana goyo baya ga yunkurin wancan shegen ciki da aka yi bari. Don kuwa ance jiragen makaman Amurka sun rinka tashi daga tarayyar daular larabawan don tafiya Isra’ila.

 

Yanzu dai wannan yunkuri yaci tura kuma ya bar baya da kura, don kuwa yanzu haka HKI nacan tana jinyar mummunan galabaitar da tayi ta kowace fuska, a Amurka kuwa tasirin Mr. Bush ya fadi kasa warwas kuma harkokin siyasarsa sun kara dagulewa, zaluncin Amurka ya kara fitowa fili, munafunci kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kara bayyana. A kasashe irin su Canada, Amurka, Ingila, Jamus da wasu da yawan kasashen turawa an fito ana tir da ‘yan Iskan da ke kokarin tallafawa nakudar cikin shegen su Mr. Bush.

 

Yanzu dai wancan yunkuri bai yi nasara ba, sai dai abin tambaya shine, shin anya kuwa akwai yuwuwar wadancan kawalai, ‘yan daudu da ‘yan tashan wancan cikin shege sun hakura. “Abin da kamar wuya” wai gurguwa da auren nesa. Sai dai yana da kyau kamar yanda al’ummar duniya ta farka don yin Allah wadai da wancan yunkuri to asake kasancewa kamar haka a nan gaba idan wadacan kawalai sun sake yunkurowa. Don kuwa wannnan wani tsohon shiri ne da yahudawa suka dade suna mafarki na samar da “israila babba”, kuma akwai yiwuwar hannun Amurka da Birtaniya dumu dumu a kokarin cimma wancan mugun kuduri na yahudawan sahayoniya. Yanzu haka ta bayyana akwai makaman da ake aiki dasu don wani sabon yunkurin, don haka yana da kyau a sa ido sosai a garesu da fahimtar duk wata manufa tasu da idon basira, tare da farkar da al’ummar musulmi akan wannan. Makaman yunkurin kuwa sun hada da Kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kamar yanda kwamitin ya zama rakumi da akala a hannun Bush da Blair. Osama bin Laden da su Ayman Al-Zawahiri duk akwai yuwar kungiyar leken asirin Amurka na amfani dasu don cimma manufofinta (watau C.I.A.), MOSSAD, tare kuma da Kharzanonin gabas ta tsakiya. Addu’a tana da tasiri ga muminai sosai, don haka a kullum kar mu manta da ‘yan ‘uwanmu Mujahidai a duk inda suke. Allah Ya taimaki Mujahidai.

 

Ga wasu muhimman bayanai a shafukan yanar gizo;

1. Bayanin Sayyid Nasrullah a ranar taron murnar nasrar Hizbullah

http://www.moqawama.org/english/_amen222.php?filename=20060926170043026

 

2.     Bayanin gargadi da jan kunnen da Dr. Ahmadinejad yayi wa taron      

majalisar dinkin duniya game da ta’addancin Amurka da HKI

(a)   na film http://www.un.org/webcast/ga/61/gastatement19.shtml

(b)  na rubutu http://www.un.org/webcast/ga/61/pdfs/iran-e.pdf

 

3.  Murnar nasarar Hizbullahi a karkashin jagorancin harka islamiyya a nijeriya

     http://www.islamicmovement.org/sheikhonhizbullah.htm

     http://www.harkarmusulunci.org/labarai19.htm

     http://www.harkarmusulunci.org/labarai19.htm

 

4.  Gargadin Sayyid Fadlullah ga Bush da Israila a hudubar juma’a

      http://english.bayynat.org.lb/FridaySpeeches/index.htm

 

5.  Imam Khamne’I (KS) ya jinjina wa Hizbullah

     http://www.alwilayah.net/qaid/labarai/qaid-zahra06.html


Sayyid Hassan Nasrullah

 


Screen Shot: Hyper Lander 2 Classic

HIZBULLAH DA SIYASAR LEBANON

 

A ranar Juma’a daya ga watan Disamba 2006 ne shugaban kungiyar Hizbullahi Sayyid Hassan Nasrullah, ya kirayi wani taron gangami tare da zanga-zangar lumana da zaman dirshan a babban birnin kasar Lebanon watau Beirut domin tilasta wa gwamnatin Firayin minista Fuad Siniora sauka daga karagara mulkin kasar, sakamakon gazawar da gwamnatin ta nuna, ko kuma tilasta wa gwamnatin amsa kiran kafa gwamnatin hadin kan kasa tare da yin garanbawul ga dokokin zaben kasar.

 

Kiran na Sayyid Nasrullah ya samu amsuwa daga dukkan ilahirin jama’ar kasar, tare da samun mahalarta daga dukkan bangarorin jama’ar kasar ta Lebanon. Wannan gangami ana gudanar da shi ne a tsakiyar birnin Beirut a dandalin ‘Martyrs’ square’ da titunan da suka nufi hedikwatar gwamnati inda Firayin Ministan Siniora da ‘yan majalisarsa suke. Masu zaman dirshan din da zanga-zangar zasu yi ta zama ne a wajan har sai gwamnatin ta amsawa kiraye-kirayen al’ummar kasar.

 

Wannan gangami dai kungiyoyin Hizbullah, AMAL Movement (Afwaj Al Muqawama Al Lubnaniyya ) da Christian Free Patriotic Movement (FPM) ne suka shirya shi. Haka kuma tsarin mulkin kasar Labnon ne ya basu wannan ‘yanci domin zabawa kasarsu kyakkyawar makoma da kareta daga fadawa hannun ‘yan baranda. Sun bayyana gwamnatin ta Siniora da kasancewar gwamnati ce dake wakiltar jam’iyya daya (March 14th Alliance karkashin jagorancin Saad Hariri). Haka kuma sun soki gwamnatin da kasancewa rakumi da akala a hannun shaidanun duniya; Amurka, Isra’ila da Faransa. Tun da farko dai masu adawar sun kirayi gwamnatin da ta yarda a hada gwamnatin hadin kan kasa inda kowace al’umma na bangarorin kasar zasu samu wakilci, amma sai gwamnatin tayi kunnen uwar shegu da wannan zabi da aka bata. Haka ne yasa masu adawar suka mika wannan kira ga al’ummar kasar domin su yanke hukunci. Bayan wakilan wadan nan kungiyoyi sun janye daga wakilcin majalisar dokoki da ajiye mukaman da suke rike dashi a majalisar Ministoci.

 

Akwai dai kwararan dalilai baya ga wancan na baya da suka tilasta yin wannan yunkuri, domin kare kasar ta Lebanon daga fadawa makirce-makircen ‘yan baranda. Daga ciki kuwa akwai cewar gwamnatin ta Siniora ta gaza wajan kare jama’ar kasar da kuma cika alkawuran da tayiwa jama’ar kasar, tana maida hankali ne kawai ga bukatun ‘yan baranda. Sakamakon hakan ne ya sanya bashin dake kan kasar ta Lebanon ya hau sama da dalar Amurka $44 biliyan. Ga kuma sayar da masana’antun kasar mallakar gwamnati ga ‘yan baranda da gwamnatin keyi. Rashin aikin yi ya hau da kusan kashi 18%, rahoton musamman kuma ya tabbatar da cewa kusan kashi 75% na mutanen kasar na cikin zaman talauci. Gwamnatin ta gaza samar da tsaron dukiya da rayukan jama’ar kasar, wannan ne ya kara haifar da kashe-kashe da tashin bama-bamai a cikin kasar ta Lebanon. Gwamnatin dai ta kara nuna gazawarta musamman akan kira da shugabannin kasar keyi ga ‘yan baranda da suzo su kafa hukumar binciken wadacan kashe-kashe da akeyi a cikin kasar. Kungiyar Hizbullahi kuma ta zargi gwamnatin da yunkurin biyan bukatar gwamnatin Amurka da Isra’ila na raba kungiyar da makamanta tare kuma da yin leken asiri ga kasar Isra’ila a lokacin yakin da kungiyar ta gwabza da HK Isra’ila.

 

Gwamnatin ta Siniora ta kuma nuna gazawa kan kin tura sojojin na Lebanon su kare kudancin Lebanon a lokacin yakin, sai shi Siniora ya buge da ‘yan koke-koke a gaban taron kasashen larabawa. Siniora kuma ya gaggauta yarda da kudurin Majalisar Dinnkin Duniya (MDD) tare kuma da sanin cewa kudirin bai dace da bukatun kasar ta Lebanon ba, yama bada dama ne da suka dace da abinda HKI suke hankoron cimmawa. Ya yarje da ajibge sojojin MDD da na NATO  a gabar kasar wadanda zasu yi aiki don kare HKI ba wai kasar tasa ba. Babbar manufar jibge wadan nan sojojin shine samun damar takawa Hizbullah birki tare da kange duk wata hanya da ake jin za’ayi amfani da ita don shigowa da makamai ga kungiyar. Shawagin da jiragen HKI suka rinkayi a sararin samaniyar Lebanon ya kara tabbatar da kasancewar sojojin grkuwa ga HKI duk kuwa da hakan ya sabawa kudirin MDD mai lamba 1701.

 

Haka kuma tun bayan gama yakin da akayi da HKI da Hizbullah, gwamnatin ta Siniora ta kasa samar da wani tallafi ga wadanda suka yi asara a lokacin wancan yakin. Babu kuma wani yunkuri na sake gina kayan jin dadin rayuwa da gwamnatin tayi zuwa yanzu. A lokacin da Hizbullah ta alkawarta biyan diyya ga wadanda akayi wa barna a lokacin yakin, tana kuma cika alkawarin kawo yanzu, ita kuwa gwamnatin sai ta buge da yawo da kokon bara ga kungiyoyin “Paris”  don tallafin kudin da zata fara irin wancan aikin da tuni Hizbullahi suka aiwatar. Bashin dai da gwamnatin ta Siniora take nema yana tare da sharudda na siyasa, takunkumai tare da tarin riba da ruwa a lokacin biya.

 

A daya bangaren kuma gwamnatin ta Siniora da magoya bayanta irin su Amurka da Isra’ila suna zargin hannun Iran da Siriya kan faruwar wannan guguwa ta siyasar Lebanon. Ga masana tarihin al’ummar Lebanon wadanda suke cike da hamasa, kishin kasa da sadaukar da kai kaskanci ne wannan a garesu a alakanta su da kasa yin komi sai da izinin wata kasa. Suna zargin Siriya da Iran da maida kasar ta Lebanon a matsayin dandalin yakinsu da abokan adawa na Isra’ila da kasashen yamma ‘yan barandan Isra’ila. Suna kuma zargin Siriya da hannu a kashe-kashen siyasar da akeyi a Lebanon. Tare da kokarin tunzura masu wannan yunkurin siyasar maida martani don canza akalar gangamin. Har wala yau suna kuma kokarin fassara wannan gangami da salon juyin mulki daga ‘yan shi’a  ko rikicin shi’a da sunna kamar yanda kafafen yada labaran yammacin duniya da Amurka suke ta kokarin shelantawa. Duk da kasantuwar mabiya kowane bangare (sunna, shi’a da kiristoci) a cikin wannan gangami na masu adawar da gwamnatin ta Siniora.

 

Kashe-kashen siyasar dai na Lebanon, uwar shedanu Amurka da HKI aka fi zargi da hannu a ciki musamman kama wasu makamai da ake kisan mummuke dasu da jami’an kwastam na Lebanon suka yi, wadanda aka aiko wa wani tsohon soja kuma jami’in ofishin huldar jakadancin Amurka.

 

Irin wannan yunkuri na gangami ne dai aka taba gudanarwa a kasar ta Lebanon a watan March na shekaraar 2005 inda aka kifar da gwamnatin Firayin Minista Omar Karami mai goyon bayan Siriya, wancan yunkurin kuma ya samu goyon bayan Amurka da kawayenta, inda suka shelanta goyon bayansu da cewar yunkurin ya dace da tsarin dimokaradiyya. Sai dai a koda yaushe suna goyon bayan abinda ya dace da manufofinsu ne, domin kuwa a wannan karon sai gashi suna kurarin cewar matukar wannan yunkuri ya kifar da gwamnatin Siniora, to zasu janye duk wani tallafi tare da yanke duk wata hulda da kasar ta Lebanon.

 

Wani dalili da yasanya kasar Amurka da na yammacin duniya suka yi wa Lebanon zuru suna kuma kokarin juya kasar yana da nasaba da kasantuwar kasar mai iyaka da HKI, ga kuma kasantuwar Hizbullah mai karfin makami da ikon fada aji ga al’ummar kasar ta Lebanon. A tsarin wannan gwamnati, kungiyar ta Hizbullah bata da ikon fada aji ta hannun wakilanta domin basu kai biyu cikin uku na ‘yan majalisar ba. Ta janibin goyon baya kuma, al’ummar kasar suna tare da kungiyar, wannan gangami da ake aiwatar wa ya kara tabbatar da hakan. Idan kuma tafiya ta tafi wannan yunkuri na iya canza tsarin siyasar kasar. Wannan ne kuma hanya mafi sauki ta kauda ‘yan koren kasashen yamma da Amurka daga karagar mulkin kasar. Faruwar hakan ne suke tsoro shi yasa suke ta kokarin shafa kashin kaji ga wannan yunkuri tare da kiran gangamin da sunaye daban-daban.

 

Shugaban Hizbullah Sayyid Nasrullah kamar dai yanda ya saba yin alkawari da cikawa, a wannan karon ma ya yi alkawarin nasara ga masu gangamin da taimakon Allah. Kamar yanda yace, gangami ne na lumana, ba yunkuri ne ba na ture wani bangare daga cikin gwamnati ba, a ‘a yunkuri ne na samar da gwamnatin hadin kan kasa inda kowa zai samu wakilci da bada gudunmuwa wajan tsara manufofin kasa. Ya kara da cewa hakan ya zama dole don kwace igiyar siyasar Lebanon da ‘yan baranda ke juyawa daga wajen kasar.

 


Screen Shot: Project BOB

TA’ADDANCI DA ‘YAN TA’ADDA: TAMBAYOYI GA MISTA BUSH

 

                     Tun bayan harin da aka kai wa dogayen ginin cibiyar kasuwanci ta Amurka (world trade centre)  da cibiyar tsaro ta Pentagon a ranar 11 ga watan satumban 2001, sai kawai naji  Mista Bush ka  bayyana cewa ai ba kowa keda alhakin yin wannan aiki ba sai Osama bin Ladin da kungiyarsa ta Alqa’eda. Wannan ne yahaifar da yunkurin yaki da ta’addanci da gwamnatinka Mista Bush da ‘yan korenka suka shelanta. Musamman al’ummar musulmin da suka rasa rayukansu Allah kadai ne yasan iyakarsu da sunan wannan yaki na ta’addanci da kace kana yi.

                    Ba ina nufin in baka labarin abinda ya faru bane a baya, a’a ka fini sanin musabbabinsu da abinda ake son a cimmawa sai dai dole ne in kawo wasu abubuwa da suka faru a takaice domin sune jigon tambayoyin da nake son in yi maka Mista Bush.

                    Mista Bush bayan ayyana wannan shelar keda wuya kawai sai naji kana neman gwamnatin ‘yan Taliban ta Afghanistan ta mika maka Osama ka hukuntashi, Kiyawarsu akan wannan bukata taka ita ce ta kaika yaki da gwamnatin ta ‘yan Taliban. Ba da dadewa ba kuma sai naji ka shelanta fara wani yaki, saima naji wai zaka tura rundunar sojojinka zuwa gabas ta tsakiya, sai dai wannan ba Afghanistan zasu ba sai naji wai Iraki zasu. Tun ina jin wai wai sai kawai naji ka tura sojojinka Irakin da nufin neman makamai masu linzami wanda kace wai cikin ‘yan dakikoki za a iya harbosu su iso gareka, don haka kace ba zaka jira haka ta faru ba zaka shigo Irakin ka kwato su da kanka. Kamar almara sai kawai naji Saddam ya shiga zana ko kasa ko sama, amma daga baya sai naji ance kun kamo shi cikin rami kamar wani zomo. Amma daga baya sai naji kana cewa baku sami wadannan makamai ba kuma kun tabbatar da basu, kace amma zaku ci gaba da zama Iraki don samara da ‘yanci da tabbatar da dimokaradiyya.

                     Mista Bush abin day a kara daure mani kai shine a daidai lokacin da jama’ar kasashen duniya suka fito suna tofin Allah tsine da harin da kakai da kisan kare dangin da kake yi a Iraki, musamman wannan bore yafi kamari a Turai da kasashen Larabawa sai kawai naji suma bama-bamai suna tashi a kasashensu. Kasashen da bama-baman suka tsahi sun hada da Spain( Madrid),Russia(Mascow) ,Saudiyya, Lebanon, Iran, England (London) ga kuma Irakin da Afghanistan inda bama bamai suka dinga tashi a kasuwanni, tashoshin mota, jirage, masallatai dss.

                  Mista Bush shin su wanene wadannan ‘yan ta’adda masu alhakin wannan aiki ? Nasan a wurinka ba wasu bane illa musulmi, kuma ba ka tsaya akan ‘yan alka’ida kawai bane a’a kai a wurinka kowane musulmi dan ta’adda ne kuma kana shirin yakarsa kamar yanda ka fada a bayan harin na 11 satumba cewa zaka yi “CRUSADE” ne, kuma abinda muke gain kenan a yau.

                   Mista Bush duk da nasan baka cika son yawan tambayoyi ba musamman na ‘yan jarida, to saidai kayi hakuri don niba dan jarida bane sai dai a gaskiya naga kana ganin kamar bani da tunani ko bana iya gane inda ka dosa kuma wasu lamuran naka sun daure mani kai, a tsammaninka komi ka fada zan yarda, abin yana cimani tuwo akwarya, hakan yasa nayi tunanin in shirya tambayoyina kila ka iya daurewa ka bani amsa tunda ni ba dan jarida bane. Koda yake naji anyi ta zarginka cewa baka da basira kuma ma baka iya Magana ba, sai kwatsam naji wajan kamfen dinka na 2004 kace ai wannan ba laifinka bane sai aka ce ka juyo ka kalli mahaifiyarka kace “laifinki ne”  To nidai wannan ba zai karya mani karfin hali tambayoyi naba, karfin hali wai barawo da sallama.

                    Mista Bush kamar yanda naji labari nasan karigani ji kuma kafini sanin haka cewa ranar da aka kai hari a cibiyar kasuwanci a nan Amurka akwai yahudawa 5000 da ke aiki a wannan wuri amma basu zo aiki ba. Duk da kunce hari ne dab a zato ba tsammani ya faru, ance kwana biyu kafin harin firaministan Isra’ila Ariel Sharon ya soke wata ziyara da yayi niyyar kawo wa nan Amurka. Har wala yau a daidai lokacin da wannnan al’amari yake faruwa ance jami’an tsaronka sun kama wasu yahudawa a nan Amurkan suna daukar hoton al’amarin suna dariya da shewa, ance bayan kama su an sake su. Mista Bush bias la’akari da wadannan dalilai anya ba Yahudawan Sahayoniya bane suka yi wannan aiki na hare-haren nan na Amurka ba don cimma wata manufa? Sannan kamar yanda nace a baya kafini sanin duk wadanan abubuwa da na fada, anya ba ka kauda kai bane don biyan bukatun iyayen gidan naka yahudawa ba ? Tare da biyan bukatarsu ta dauke hankalin duniya daga ta’addancinsu na kisan gillar da sukewa musulmin Palasdinu ba?

              Mista Bush sanannen abu ne cewa babban jami’in cibiyar tsaronka ya tabbatar da cewa sunsan inda Osama yake sai dai kawai basa son kama shi ne a yanzu, musamman ganin cewa shi Osaman tsohon ma’aikacin maikatar liken asirin kasar ka net a CIA, da kuma ganin mu bama mu fara jin sunan sa ba sai kafofin yada labarinku. Da din dadawa nasan da cewa gwamnatin kasarka ce ta baiwa Saddam mugayen makamai don ya yaki jamhuriyar musulunci ta Iran a lokacin daya yaketa na tsawon shekara takwas (1980-1988). Har wala yau ba kubane kuka raini ‘yan Taliban a lokacin da suka kwaci Afghanistan daga hannun Rasha, kuka basu horo da makamai ? Shin baka tunanin zaiyi wahala mu iya gaskata ka akan cewar a tsakaninka da Osama/Saddam/Taliban zaman doya da manja ne kuke watau kamar annabi da kafiri tun fil azal? Ni dai ina ganin kai da ukun  fanke ne ke tunkudar buredi, watau a samu dammar fakewa da guzuma don a harbi karsana, ko kuma ma ya zamana karene ya yi wa ubangidansa haushe shine yake son maganinsa ta hanyar jifar tsuntsu biyu da tsakuwa daya idan aka yi la’akari da wadancan dalilai na baya? Ni dai abinda nake gani kenan ko kuwa ya abin yake Mista Bush ? Zan so naji gaskiya daga bakinka, ko da yake tana da wuyar fada!

                Mista Bush ba ka tunanin hujjojin da ku ke bada wa suna da rauni da rainin hankali ? Abinda yasa n ace haka harin da aka kai a birnin Madrid ance an gane maharan musulmai ne don larabawa ne har ma anbisu za’a kama sai suka shige wani gida inda daga karshe aka budewa gidan wuta aka kasha kowa, amma wai bayan an dagargaje gidan sai a ciki aka samu wasu bama-baman a cikin gidan wanda maharani suka so suyi amfani dashi. Daga baya ma ance anshici wani faifan bidiyo na yanda aka shirya harin tare da kur’ani a bayan gari abinda ke nuna dai lallai musulmi ne suka yi abin.Harin Birnin Moscow ma kunce su maharan saida suka dauki duk yanda suka yi kisan kuma duk da irin bama baman da suka tada ya kashe kowa shi faifan bidiyon bam bai iya kone shi ba? Haba Mista Bush wannan daga ji yayi kama da irin tunaninka, kana tsammanin wadannan hujjoji abin gamsuwa ne bama ga musulmai ba har ga wadanda ba musulmi ba?                               

                   Mista Bush ni na fahimci kalmar ta’addanci kana nufin musulunci,’yan ta’adda kuma musmulmai. Wannan ya fito fili a gareni ne musamman lokacin da kuka shiga garin Najaf mai tsarki kuka dinga kashe bayin Allah har kuna hankoron shiga masallacin inda kabarin Sayyidna Ali (as) yake da sunan kuna zakulo ‘yan ta’adda ! Kuma har kuka shelanta Shehun malamin nan Sayyid Muqtada Sadr a matsayin mai ayyukan ta’addanci.kuma sojojinka sun yi ruwan wuta ga musulmi a ranar Ashura 1426 da sunan dai yaki da ta’addanci. Mista Bush bana tunanin babu hannunku a cikin tashin bama-baman da suka kashe babban malamin nan Sayyid Bakir Alhakeem (R) musamman in akayi la’akari da wadancan ta’addanci da sojojinka suka yi .Dubi irin luguden asojojinka sukayi wa garin Fallujah ! Shin wannan bai nuna musulunci kake nufi ba a zahiri?

                  Mista Bush bana jin mutanen kasarka da ma sauran duniya suna ganinka a matsayin gwarzo akan yakin da kace kana yi da ta’addanci, domin kuwa kullum abinda ake gudun ne ke ta kara faruwa.Kullum kana kara jefa duniya cikin firgici da zullumi, maimakon yakin da ta’addanci sai abin ya zama tamkar janyo karuwar ayyukan ta’addancin ma kake.Na ga irin yanda sojojinka keta luguden wuta a birane da kauyukan kasar Iraki da Afghanistan inda ake ta kashe tsofaffi,yara da mata, anata rushe gidajen talakawa da sunan yaki da ‘yan ta’adda. A zahiri Mista Bush bana iya banbamce Iraki ko Afghanistan da Palasdinu musamman in ina kallon labaran talabijin ta fuskacin kisan gilla da ta’addanci da rundunarka suke. Abin sai nake ga kamar sojojin Isra’ila suka ba sojojinka horo. Mista Bush abinda nake son tambayarka anan anya wannan kisan kare dangi da kake a wadannan kasashe na musulmi ba umarni kake samu ba daga iyayengidanka su Sharon na Isra’la ? Musamman ganin cewa sune suka taimakeka ka kai ga kan wannan kujera a karo na farko da na biyu na zaben da suka gabata, kuma ganin cewa su yahudawan suna da kudurin mamaye dukkan kasashen musulmi na gabas ta tsakiya. Shine nake ganin anya ba wannan wani shiri bane kuke don ramawa kura aniyarta ? Watau wata kila ko kayi masu alkawarin kama masu Irakin akan wancan shiri nasu. Abinda yasa nace maka haka shine ganin yanda kake ta janyo asara na rayukan sojojinka gashi kuma yakin babu riba a gareka in banda raba yara da iyayensu kasa ana ta kashesu ba gaira bare dalili.

               Har wala yau Mista Bush zanyi maka wata tambaya wadda nasan baka cika son ayi maka ita ba, sai inga kana ta inda-inda da ‘yan kame-kame da zaran anyi maka ita. Kace kunshiga Iraki neman makamai ne, da ta tabbata babu makamai kaki ka fita kace wai zaku samar da ‘yanci da dimokaradiyya ga mutanen kasar ne. To in har haka ne shin abinda kukayi a gidan kurkukun Abu Ghraib na Irakin inda kukayi ta tilasta musulmi suna shan giya,naman alade tare da yi masu tsirara da yiwa mata fyade. Mista Bush dama haka irin ‘yanci da kake ta fada yake? Wannan shine dimokradiyyar da kayi alkawari. Bayan wannan sai naji wani sabon cin mutunci kuma ga Alqur’ani maitsarki a kurkukun Quantanamo.Anya wannan ba yakin nan bane da kace zakayi na “CRUSADE” ? In ba haka ba ina hujjojin da zaka kare kanka akan wannan ?

               Zan barka anan kayi nazarin tambayoyina amma daga karshe zanso kasani cewa, abinda kake yi tarihi ba zai manta da kai ba a matsayin wanda ya jefa al’ummar duniya cikin rikici,talauci,yaki da nau’o’in firgici da tashin hankali kala-kala,kuma komi ne ne zaka shirya a boye to akwai lokacin da duniya zata fahimta kuma tayi tofin Allah ya tsine akanka, wannan kuwa in ta bayyana har wasu daga mutanen kasarka sai sun bi sahun yi maka tofin Allah tsine don ka jefasu cikin tsoro da firgici maimakon kula da matsalolinsu na rayuwa.

        Naji dayawan mutane basu da wurin kwana a Amurka suna kwana a titi , wasu ba aikin yi shi yasa suke shiga harkar kwaya da shaye shaye ko su zama ‘yan daba, ance akwai tsadar rayuwa a kasarka kuma mutane suna ta kuka akan wannan. Amma sai ka zabi yaki akan maganin matsalolinsu.Mista Bush duk wanda baibar tarihi na kwarai ba a rayuwarsa a duniyar nan to yayi asara. Ina fatan ko a makaranta an dan taba baka labarin azzalumai irin su Hitla na jamus, Stalin na Rasha, Mussolini na Itali, kuma baka rasa sanin mugaye irinsu Sani Abacha, Shah na Iran kai Saddam ma aya ne gareka inda kana idirakin al’amura.

           A tarihin musulunci ba a koyar da musulmmi sanya wa al’umma bama-bamai ba. Ko da ma yaki ake ah hanamu kashe yara da mata da tsofaffi, bare kuma muje mu dinga sanya bam yana kashe mutane.Muna da tausayi ba ga mutane ba har da dabbobi bare kuma mutane, addininmu bai koya mana wannan rashin imani ba, fatar mu Allah ya tona asirin masu wannan ayyuka na ta’addanci, masu sanya bam suna kashe mutane koda kuwa yaranka ne (CIA/FBI) kuma koda MOSSAD na Isra’ila ne kai koda ma KGB na Rasha ne, idan ma ‘yan ta’addan ne daga musulmi to Allah ya tona masu asiri duniya ta fahimci gaskiyar al’amarin.

             Sai naji daga gareka.

                                                               


Marigayi Imamu Khomaini

 


Bayahude dan ta'adda

 


Imam Aliyu Mazan Fama

 


Imamu Khomain (r)

 


Shahid Ahmad Yasin

 


Shehu Zabin Allah: Zakzaky