Shahidan Karbala

Shafin Farko | ENGLISH PAGE | Shafukan malamai | Littafin maziyarta | Hotuna | Tuntuba | Siyasar Muslunchi | Shahidan Karbala | Photoalbum

Screen Shot: Hyper Lander 2 Classic
HUR BIN YAZID ar-Riyahi (R) 
 
 A ranar 9 ga watan Muharram, kwamandojin sojin Yazidu (LA) suka fara kada kugen fara yakar Imam Hussain (AS) dan Fatima az Zahra diyar Manzon Allah (s.a.w.a.). Imam Hussain ya kira dan’uwansa Abbas a daidai wannan lokaci yace masa “ya Abbas! kaje ga kwamandojin sojojin Yazidu, ka tambayesu su yi mana Karin jinkirin dare daya, har zuwa gobe”. Abbas ya tafi zuwa ga wannan bukata ta Imam Hussain. Hakan kuwa ta samu.
          Shin Imam Hussain yana neman Karin jinkiri ne domin kara samun damar ganawa da iyalansa? musamman karamar diyarsa Sakinah da bata iya barci sai akan kirjinsa? Amsa dai shine a’a, ko alama ba haka abin yake ba. Ai Imam Hussain yana neman Karin jinkirin lokaci ne domin Karin munajati da ubangijinsa da kuma jiran wani bakonsa na musamman; HUR BIN YAZID.
          Hur shine farkon kwamandan sojojin Yazidu wanda ya fara tare Imam Hussain ya hana shi wuce wa zuwa Kufah. Ya tilasta wa Imam Hussain yada zango a Karbala. Ma’anar Hur shine ‘yantacce, ya ‘yantar da kansa daga wuta tun kafin lokaci ya kure. Hur ya koya mana muhimmin darasi a rayuwa. Ya kasance yana fuskantar zabi tsakanin wuta da aljanna, tsakanin gaskiya da bata, tsakanin zalunci da shiriya, tsakanin duniya da lahira, tsakanin shahada da matsayin gidan duniya. Amma sai Hur ya zabi aljanna akan wuta, gaskiya akan bata, shiriya akan zalunci, lahira akan duniya, shahada akan duniya, ya yarje ya tafi wajan Allah yana shahidi madaukaki da rayuwa cikin zilla.
          A yau cikin rayuwar da muke muna iya fuskantar ire-iren wadannan kalubale da Hur ya fuskanta, don haka tarihin rayuwar wannan bawon Allah Hur bin Ziyad ya koya mana irin zabin daya kamata muyi.
          Ranar 9 ga Muharram ta kasance rana mafi tsanani daga cikin ranaku na bakin ciki musamman kasantuwar ita ce rana ta biyun karshe a duniya ga Imam Hussain da sahabbansa, ita ce ranar da tafi sauran ranakun da suka gabace ta tsanani kan musgunawa da cutarwan da aka yi wa Imam Hussain da Iyalansa da wadanda suke tare da shi. A wannan rana yara kanana sun rinka kuka suna kiran ruwa saboda kishirwan da ke damunsu, suna cewa ‘Al-atash! al-atash!, al-atash!’ Wannan kuka na kananan yara ya rinka isa har kunnuwan sojojin Yazidu da suka hana su koda makwalwa daya na ruwa daga kogin Furat.
          Wannan sauti mai tada hankali ya rinka isa har kunnuwan Hur, wanda a daidai wannan rana yana cikin sojojin Yazidu, hakan yasa hankalinsa ya rinka tashi, yana tunani cikin zuciyarsa, yana Magana da ita kan kuskuren day a aikata. Hur yana cewa “mi ya ja mani? Mi yasa? Mi yasa na sanya dan Fatima a wannan matsayi? Shin Hussain zai yafe mani? Allah zai yafe mani? Yaya zan yi na nemi gafara?”  A haka dai Hur ya share wannan dare yana ta tunani, yana kuka da neman gafarar Allah akan wannan kuskure da yayi.
          Ranar 10 ga Muharram dokunan sojojin Yazidu, tun kafin fara yaki suka fara tsalle, basu iya tsayawa a wuri daya saboda tsananin zafin rana da ke damunsu a kofatonsu. Sojojin Yazidu suka fara debo  ruwa daga kogin Furat suna zubawa kafafu da kofaton dokunansu domin su samu saukin zafi.
          Hur sai ya fara tsunduma cikin tunani akan abinda yake gani da idanunsa, a lokacin da yake jin kukan Iyalan Manzon Allah saboda kishirwa sai yaga ana zuba ruwa ga dokuna domin suji saukin zafin rana a kafafunsu. Hur yana tunani a ransa “ruwa mai yawa ga dabbobi, alhalin ‘ya’yan Sayyida Fatima suna kuka kan ruwa dan kalilan. Za’a iya baiwa dabbobi ruwa mai yawa, amma jikokin Manzon Allah an hana su”. Wannan zalunci ya kara firgita Hur tare da tada masa hankali.
          A haka dai Hur ya kasa jure wa abinda yake ji da gani da idanunsa na zalunci, sai ya yanke shawarar canza zabi, ya kira dansa yace “ya dana, nayi babban kuskure. Na tare wannnan mumini mai tsarki a nan don a kashe shi. Ya dana , Don Allah, ka yi sauri ka kaini wajan Imam Hussain in roki gafara a wajansa tun kafin lokaci ya kure, ina jin kunyar abin da na aikata. Shin Hussain zai yafe mani? Da wace fuskar zan fuskance shi?”
Hur yaci gaba da cewa “ya dana, kafin ka kaini ga Hussaini, ka daure mani hannayena kuma ka rufe mani fuskata, ta yanda ba zanyi ido biyu da shi ba a lokacin da nake  neman gafara.”
          Wannan da mai biyayya ya aikata duk yanda babansa ya umarce shi. Ya dauko igiya ya daurewa babansa hannaye, ya sa kyalle ya rufe masa fuska kamar yanda ya umarceshi. Ya kama igiyar yana ja  ya tafi dashi gaban Imam Hussain.
          Abul Fadl Abbas, babban kwamandan Imam Hussain, yana tsaye ya hango mutum biyu na nufo inda suke daga rundunar Yazidu, sai ya fitar da takobinsa daga kubenta yana gargadinsu da su tsaya inda suke. Imam Hussain yana kallon abinda ke faruwa, sai ya taho zuwa ga Abbas yana cewa “Ya dan’uwana Abbas! mai da takobinka, wadannan mutane ba sunzo yakarmu bane. Hur  ne bako na na musamman , shi nake jira, muje mu karbesu ya Abbas!” Imam Hussain da Abbas suka kama hanya domin tarban wadannan baki nashi. Suna isa Imam Hussain yace “sannu da zuwa Hur, Ina ta jiranka.” Hur ya fadi bisa kafafun Imam Hussain yana cewa “Ya shugabana, ka yafe mani don Allah, don Allah ka yafe mani, ina mai matukar nadamar abinda na aikata, ya kaicona.”
          Imam Hussain ya kama kafadun Hur, yana ce masa “Hur, ya abokina  na yafe maka, ina tabbatar maka cewar Kakana, Babana da Mahaifiyata sun yafe maka, taho gareni ya Hur.” Suka kama hanya zuwa sansanin Imam Hussain.
          Hur yayi zabi mafi inganci, ya samu Imam Hussain mai yawan afuwa da gafara, Hur ya zabi zama ‘yantacce maimakon zinari da dirhamomi ko zama a cikin kaskanci da azaba mai tsanani gaban Allah Ta’ala gobe kiyama.
          Bayan Imam Hussain ya jagoranci sahabbansa da iyalansa sallar azahar, sai maita da kwadayin fara yaki ya kara tsananta daga Yazidawa, suka ci gaba da kada kugen yaki da yunkurin kawo hari. Hur kuwa ya kasance cikin shauki da kwadayin kasancewa na farkon wanda zai fara shiga filin yaki yin mubaraza domin kare Hussaini dan Fatima al- Zahra (as).  Don bada kariya ga addinin Allah, sai Hur ya fara neman izini daga Imam Hussain.
          Imam Hussain yace masa “Ya Hur kai bako na ne, ka kasance tare dani na lokaci ne dan kalilan. Ban samu nayi maka  hidima yarda ya kamata ba, ban iya na baka ko ruwa ba bare abinci. Kadan zauna tare dani mana koda dan kadan ne mana akalla. Ya Hur kai bako na ne , ba zan bari a kasheka ba.”
          Hur, babu abin da zuciyarsa take hange sai daukakar da zai samu gobe kiyama idan har ya rabauta da samun shahada a wannan rana. Yana tunanin girman matsayin bada rai domin kariya ga dan Manzon Allah, musamman a irin wannan rana kuma a wannan wuri, don haka sai ya kasa hakura yaci gaba da rokon Imam Hussain akan bukatarsa. Imam Hussain ya fara tunanin idan Hur yaci gaba da zama tare da su, to zai fuskanci irin matsalar da ake fuskanta a sansanin ta fama da kishirwa da yunwa, don haka Imam Hussain ya amsa wa bukatar Hur, aka bashi izini, ya kama masa ya hau dokinsa.
          Hur dama ya kasance jarumi ne, don haka Yazidawa basu ji dadi ba a hannunsa, don haka sai da suka yi masa taron dangi, suna sara da takubba, suna jifa da masu kuma suna harbi da kibau. Raunukan da suka ji masa yasa ya fado akan dokinsa jina-jina ya fadi kwance yana kiran Imam Hussain “ya shugabana! zo da sauri, ko na samu ganinka na karshe!”
          Imam ya rugo ya dauke shi ya kwantar da shi a cinyarsa, yana masa bushara da cewa, Manzon Allah (S.A.W.A.) da Sayyida Fatima  (A.S)                    suna jiran tarbansa. A wannan hali Hur ya tafi zuwa ga Ubangijinsa yana yardajje, ‘yan tacce wanda bai yarda da zama a cikin zilla ba. Imam Hussain da Abbas suka dauki gawarsa suka kai sansanin Imam Hussain. Inna Lillahi wa inna Ilaihi raji’un.

HADIMIN IMAM HUSSAIN JAUN (R)

Daga cikin sahabban Imam Hussain (AS) wadanda suka sadaukar da rayuwarsu don kare addinin Allah da taimakawa Iyalan Manzo ‘ya’yan  Fatima az- Zahra (AS), jarumai kuma zababbaun Allah, a cikinsu akwai hadimin Imam Hussain (AS) wanda ake kira Jaun (R).
          Jaun wani bawa ne ga Abu Zarril Ghifari sai shi kuma yayi kyautarsa ga Imam Ali (AS) da Sayyida Fatima (AS), ya rayu a tare da su har zuwa lokacin da Imam Ali ya yi shahada. Daga sai ya kasance karkashin Imam Hassan Al-Mujtaba. Ya zauna tare da shi har lokacin da Mu’awiya ya bashi guba ya yi shahada. Bayan wannan lokacin ne ya koma karkashin Imam Hussain, ya kasance tare da shi har zuwa lokacin da ya yi shahada a Karbala. Jaun bakar fata ne dan asalin Habasha, ya kasance mai yawan ibada gashi kuma mahaddacin AlKur’ani malamin tafsirinsa masanin hadisan Manzon Allah, sakamakon zamansa da Imam Ali da ‘ya’yansa guda biyu tsarkaka na tsawon lokaci a rayuwarsa.
          Imam Hussain ya nunar da dukkan wadanda suke tare dashi a Karbala cikin daren Ashura cewa, idan sun so suna iya tafiya abinsu, ya sahhale masu, domin makiya shi suke son kashewa. Amma salihan bayin Allah daga cikinsu suka kasa tafiya. Jaun samu yarjewar Imam Hussain kan ya tafi idan yana bukata amma Jaun bai kasance cikin wadanda zasu iya tafiya su bar ‘ya’yan Sayyida Fatima a tsakiyar makiya ba.
          Jaun ya fahimci hakikanin matsayin Imam Hussain, ya fahimci sakon da ya ke son isarwa ga al’ummar kakansa. Don haka sai Jaun ya zabi yayi tarayya da Iyalan Manzo (AS) akan wannnan aiki. Ya kasance tare dasu a cikin lokuta masu dadi, don haka sai ya zabi yaci gaba da kasancewa tare dasu har a lokuta masu wahala na rayuwarsu.
          Lokacin da Imam Hussain ya shirya barin garin Madina don fuskantar kudurar Allah da take jiransa, don gagarumin aikin daukaka addinin Allah, sai Jaun ya roki Imam Hussain da ya tafi  tare dashi a wannan tafiya mai albarka. Kauna da matsayin Jaun wurin Iyalan Manzo yasa Imam Hussain ya amince masa.
          Bayan makiya Manzo (S.A.W.A.) sun tare Imam Hussain a Karbala tsawon kwanuka tara, a daren goma ya kasance wani muhimmin dare a wurin Jaun, yana shaukin idan gari ya waye zai fafata kuma ya sadaukar da rayuwarsa domin kariya ga masoyansa, ‘ya’yan Sayyidah Fatima (AS). Jaun ya share dare yana wasa takobinsa a lokaci guda kuma yana karatun Kur’ani.
          Ranar goma ga Muharram kuwa ta kasance rana ce ta masifa ,kunci da tsanani ga masoyan Imam Hussain. Ga rana, ga yunwa ga kuma sojojin Yazidu a gefe suna ta buga gangar yaki. Bayan Yazidawa wajan su dubu talatin sun fara kawo farmaki ga rundunar Imam Hussain mai mutane 73 duk da shi, aka fara gwabzawa. A cikin wannan yanayi mai ban tausayi da sosa zukata Jaruman sahabban Imam Hussain suka fara shahada bayan sun aika da daruruwan Yazidawa jahannama. Haka aka ci gaba da wannan yaki har zuwa bayan sallar Azahar. Sai Jaun ya matso kusa da shugabansa Imam Hussain cikin natsuwa yana tallabe da hannayensa, ya yi shiru! Da gani babu tambaya akwai abin da ke damunsa, yana son isar da abin da ke zuciyarsa ga Imam Hussain.
Imam Hussain ya kalli masoyin bawansa cikin tausayi yace masa “Ya Jaun! Abokina Jaun! Mi ya faru ne?” Da jin haka, Jaun ya samu abin da yake jira, sai amsa da cewa “Ya shugabana! Abin ya isa haka, ba zan iya jure ci gaba da ganin wannan bakin ciki ba. Ba zan iya jure ganin ana kashe ‘ya’yan Sayyida Fatimah a idona ba. Ya shugabana don Allah! Ka bani izini in shiga filin fama.” Allahu Akbar, sai Imam Hussain yace masa “Ya Jaun! Kai tsoho ne. Jihadi bai zama wajibi ga tsoho kamarka ba. A’a ya Jaun! Ba zan bari a kashe ka ba.”
Jaun yaci gaba da neman yardan Imam Hussain akan wannan bukata tashi ta ya yarje masa ya shiga ya yi arangama da makiya Allah rundunar Yazidu (LA). Karshe dai Imam Hussain ya amince masa da hakan, ya kuma kara shiri Imam Hussain ya kama masa ya hau dokinsa yana ,asa addu’a, ya kama hanya sai wajan sojojin Yazidawa.
Jaun ya kama hanya ya nufi tsakiyar fili don bada kariya da sallama sauran mintunan da suka rage mashi na rayuwa zuwa ga Allah. Ya tafi yana tuna zamansa da Manzon Allah (S.A.W.A.), yana tuna kaunar da ke tsakanin Manzon Allah da wannan masoyin jika nasa Hussain. Jaun ya tuna lokacin da Manzon Allah (S.A.W.A) yana jan salla a masallaci Hussain yana karami yazo ya hau bayan Manzon Allah, sakamakon hakan sai da Manzo ya dade bai dago daga sujada ba, har sai da Hussain ya sauka sannan ya dago, Manzon Allah baya son cutar da Hussain don kuwa wannan hani ne daga Allah Ta’ala. Jaun ya tuna lokacin da Hussain yake karami in yana wasa yaji rauni Manzon Allah ne dakansa ke kula dashi. Haka Jaun yaci gaba da tunanin matsayin Imam Hussain da kaunar da Manzon Allah ke masa. Yana cikin tafya, sai ya daga sautinsa yana  cewa makiya Manzon Allah Yazidawa, sojojin Yazidu “Ku dubeni! Kun sha ganina tare da Manzon Allah. Ku tuna Manzon Allah mana ta hanyar ganina. Kunce kunyi imani da Manzon Allah, kun kira kanku musulmai, shin kuna tsammanin Manzon Allah zai yi murna da ku kan kashe jikansa?” Jaun yaci gaba da cewa “Mi Hussaini ya yi maku ne? Bai yi maku laifin komi ba, ku kyaleshi. Ku tseratar da kanku daga wuta.”
Wadannan sojoji na Yazidu (LA) shaidan ya yi masu hudubar da ba zasu saurari kiran duk wani mai kira ba, don haka ba zasu karbi wannan kira daga salihin bawan Allah ba. Maimakon haka ma sai suka rugo suna gagugawa domin zubar da jinin Jaun. Suka fara sararsa da takubba, suna suka da mashi ga harbi da kibiya! Duk da haka wannan Jarumi jaun sai da ya kashe daruruwa daga cikinsu. Kishirwa da yunwa na tsawon kwana uku sun galabaitar da Jaun baya ga raunukan da Yazidawa suka yi masa, hakan ya tilasta wa Jaun fadowa daga kan dokinsa. Ya fado cikin jini, yana kira yana cewa “ya shugabana taho gareni ko na samu damar ganinka na karshe!”
Allahu Akbar, Imam Hussain yana jin wannan kira daga masoyinsa, hadiminsa kuma salihin bawon Allah sai ya rugo a guje zuwa inda Jaun yake kwance cikin jini. Imam Hussain ya dauke shi ya dora bisa cinyarsa, hawaye na zuba a idanun Imam Hussain yana cewa Jaun “Ya Jaun! Ina mai baka hakuri! Gashi zaka bar gidana ba tare da na baka abinci ko ruwa ba har kwana uku. Ya Jaun! Don Allah ka yafeni!” Allahu Akbar, Jaun yana kallon Imam Hussain sai yace “ Ya shugabana! Don mi zaka damu? Ka riga kayi mani babbar alfarma na bani dama na sadaukar da rayuwata ga musulunci” Yaci gaba da cewa “Duba, ya shugabana, dubi wadanda suka zo tarbana, Manzon Allah da kansa, Sayyida Fatima ma gata nan. Shugabana Ali da Hassan duk gasu nan!” Allahu Akbar a haka Allah ya amshi Jaun yana mai samun yakini. Ya tafi ga mahaliccinsa zababbe, yardajje kuma cikin izza da daukaka. Inna lillahi wa inna Ilaihir Raji’un.

More information about Hyper Lander

Can you give me any clues for conquering Hyper Lander? Practice developing your flying technique, the key is flying smoothly and learning to use the two engine thrusters correctly. Will you make another sequel to Hyper Lander? The story has some wrinkles which haven't been explored yet so it is likely that a sequel will be produced in order to address them. Keep checking the site for new updates.

How does the Internet figure into game development?
Typically if you have wanted to play a particular game then you have had to go to a software store and purchase a box which contains CD-ROM's or floppy disks. Games are packaged this way because the data which makes up most games takes up so much space and because physical stores have been the only place to showcase them. This data can take the form of graphics, sounds, character files, help, and of course the game engine itself. Now with the gain in popularity of the Internet, gamers don't have to get a game from a physical store, and in some cases they don't even have to install a game on their own computer. One of the contributions of the Internet to gaming has been games which exist entirely online. Project BOB is an example of this kind of game. It's graphics and code exist on the web and are expressed through a web browser. This means that updates are easier to distribute to fans of a game who visit a central storage for the game each time they log on to play it.

Screen Shot: Project BOB Bob
BOB is a full-function arcade game, using the keys seen at the left (which you can redefine). BOB is programmed entirely in HTML/JavaScript and has 36 different screens and 3 different enemies, 2 of which move. The image at the left shows keys and doors, which are dynamic---once you get them, they're gone (until the next game!). Try BOB out, or read more about creating Bob in the About and What's New section.

More information about BOB

Only 32 images are used to create BOB (six images are for BOB himself). The data that draws BOB has over 3:1 compression (but is on the same page). BOB works on all computer platforms using a proper browser (it even works on a Unix workstation -- there are special automatic adjustments for speed on HP workstations). BOB does not rely on any Applets or CGI Script pushing. The page of BOB is about 25kb, and the images for BOB are less than 7kb (most average pages have over 30kb).